Hausa - Surah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) | المكتبة الإسلامية صدقة جارية عن المغفور لهم بإذن الله أحمد سليمان البراك وزوجته وابنائه سليمان ومحمد ويونس وابنته إيمان

,,

اللهم اجعل هذا العمل نافعاً لصاحبه يوم القيامة

ولمن ساهم وساعد بنشره

,,

Surah An-Nazi'at ( Those who Pull Out )

Select reciter

Hausa

Surah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya count 46
Facebook Twitter Google+ Pinterest Reddit StumbleUpon Linkedin Tumblr Google Bookmarks Email
وَالنَّازِعَاتِ غَرْقًا ( 1 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 1
Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.
وَالنَّاشِطَاتِ نَشْطًا ( 2 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 2
Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.
وَالسَّابِحَاتِ سَبْحًا ( 3 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 3
Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.
فَالسَّابِقَاتِ سَبْقًا ( 4 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 4
Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umurnin Allah) kamar suna tsẽre.
فَالْمُدَبِّرَاتِ أَمْرًا ( 5 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 5
Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni.
يَوْمَ تَرْجُفُ الرَّاجِفَةُ ( 6 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 6
Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.
تَتْبَعُهَا الرَّادِفَةُ ( 7 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 7
Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.
قُلُوبٌ يَوْمَئِذٍ وَاجِفَةٌ ( 8 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 8
Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.
أَبْصَارُهَا خَاشِعَةٌ ( 9 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 9
Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.
يَقُولُونَ أَإِنَّا لَمَرْدُودُونَ فِي الْحَافِرَةِ ( 10 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 10
Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?
أَإِذَا كُنَّا عِظَامًا نَّخِرَةً ( 11 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 11
"Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?"
قَالُوا تِلْكَ إِذًا كَرَّةٌ خَاسِرَةٌ ( 12 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 12
Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!"
فَإِنَّمَا هِيَ زَجْرَةٌ وَاحِدَةٌ ( 13 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 13
To, ita kam, tsãwa guda kawai ce.
فَإِذَا هُم بِالسَّاهِرَةِ ( 14 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 14
Sai kawai gã su a bãyan ƙasa.
هَلْ أَتَاكَ حَدِيثُ مُوسَىٰ ( 15 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 15
Shin, lãbãrin Mũsã ya zo maka?
إِذْ نَادَاهُ رَبُّهُ بِالْوَادِ الْمُقَدَّسِ طُوًى ( 16 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 16
A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?
اذْهَبْ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ إِنَّهُ طَغَىٰ ( 17 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 17
Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.
فَقُلْ هَل لَّكَ إِلَىٰ أَن تَزَكَّىٰ ( 18 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 18
"Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.
وَأَهْدِيَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخْشَىٰ ( 19 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 19
"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"
فَأَرَاهُ الْآيَةَ الْكُبْرَىٰ ( 20 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 20
Sai ya nũna masa ãyar nan mafi girma.
فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ ( 21 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 21
Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),
ثُمَّ أَدْبَرَ يَسْعَىٰ ( 22 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 22
Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.
فَحَشَرَ فَنَادَىٰ ( 23 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 23
Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.
فَقَالَ أَنَا رَبُّكُمُ الْأَعْلَىٰ ( 24 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 24
Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."
فَأَخَذَهُ اللَّهُ نَكَالَ الْآخِرَةِ وَالْأُولَىٰ ( 25 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 25
Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَعِبْرَةً لِّمَن يَخْشَىٰ ( 26 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 26
Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.
أَأَنتُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَمِ السَّمَاءُ ۚ بَنَاهَا ( 27 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 27
Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.
رَفَعَ سَمْكَهَا فَسَوَّاهَا ( 28 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 28
Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.
وَأَغْطَشَ لَيْلَهَا وَأَخْرَجَ ضُحَاهَا ( 29 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 29
Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.
وَالْأَرْضَ بَعْدَ ذَٰلِكَ دَحَاهَا ( 30 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 30
Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.
أَخْرَجَ مِنْهَا مَاءَهَا وَمَرْعَاهَا ( 31 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 31
Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.
وَالْجِبَالَ أَرْسَاهَا ( 32 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 32
Da duwatsu, Yã kafe ta.
مَتَاعًا لَّكُمْ وَلِأَنْعَامِكُمْ ( 33 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 33
Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.
فَإِذَا جَاءَتِ الطَّامَّةُ الْكُبْرَىٰ ( 34 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 34
To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo.
يَوْمَ يَتَذَكَّرُ الْإِنسَانُ مَا سَعَىٰ ( 35 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 35
Rãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata.
وَبُرِّزَتِ الْجَحِيمُ لِمَن يَرَىٰ ( 36 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 36
Kuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani.
فَأَمَّا مَن طَغَىٰ ( 37 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 37
To, amma wanda ya yi girman kai.
وَآثَرَ الْحَيَاةَ الدُّنْيَا ( 38 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 38
Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).
فَإِنَّ الْجَحِيمَ هِيَ الْمَأْوَىٰ ( 39 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 39
To, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma.
وَأَمَّا مَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِ وَنَهَى النَّفْسَ عَنِ الْهَوَىٰ ( 40 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 40
Kuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.
فَإِنَّ الْجَنَّةَ هِيَ الْمَأْوَىٰ ( 41 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 41
To, lalle ne Aljanna ita ce makõma.
يَسْأَلُونَكَ عَنِ السَّاعَةِ أَيَّانَ مُرْسَاهَا ( 42 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 42
Sunã tambayar ka game da sa'a, wai yaushe ne matabbatarta?
فِيمَ أَنتَ مِن ذِكْرَاهَا ( 43 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 43
Me ya haɗã ka da ambatonta?
إِلَىٰ رَبِّكَ مُنتَهَاهَا ( 44 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 44
Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.
إِنَّمَا أَنتَ مُنذِرُ مَن يَخْشَاهَا ( 45 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 45
Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta.
كَأَنَّهُمْ يَوْمَ يَرَوْنَهَا لَمْ يَلْبَثُوا إِلَّا عَشِيَّةً أَوْ ضُحَاهَا ( 46 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 46
Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa.
Facebook Twitter Google+ Pinterest Reddit StumbleUpon Linkedin Tumblr Google Bookmarks Email

Select language

Select surah