Hausa - Surah Al-Fajr ( The Dawn ) | المكتبة الالكترونية لك ولفقيدك صدقة جارية عن المغفور لها بإذن الله نوره شامان الشريّد العجمي

,,

اللهم اجعل هذا العمل نافعاً لصاحبه يوم القيامة

ولمن ساهم وساعد بنشره

,,

Surah Al-Fajr ( The Dawn )

Select reciter

Hausa

Surah Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya count 30
Facebook Twitter Google+ Pinterest Reddit StumbleUpon Linkedin Tumblr Google Bookmarks Email
وَالْفَجْرِ ( 1 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya 1
Inã rantsuwa da alfijiri.
وَلَيَالٍ عَشْرٍ ( 2 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya 2
Da darũruwa gõma.
وَالشَّفْعِ وَالْوَتْرِ ( 3 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya 3
Da (adadi na) cikã da (na) mãrã.
وَاللَّيْلِ إِذَا يَسْرِ ( 4 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya 4
Da dare idan yana shũɗewa.
هَلْ فِي ذَٰلِكَ قَسَمٌ لِّذِي حِجْرٍ ( 5 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya 5
Ko a cikin waɗannan akwai abin rantsuwa ga mai hankali (da yake kange shi daga zunubi)?
أَلَمْ تَرَ كَيْفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِعَادٍ ( 6 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya 6
Ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata da Ãdãwa ba?
إِرَمَ ذَاتِ الْعِمَادِ ( 7 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya 7
Iramawa mãsu sakon ƙĩrar jiki.
الَّتِي لَمْ يُخْلَقْ مِثْلُهَا فِي الْبِلَادِ ( 8 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya 8
Waɗanda ba a halitta kwatankwacinsu ba a cikin garũruwa (na dũniya).
وَثَمُودَ الَّذِينَ جَابُوا الصَّخْرَ بِالْوَادِ ( 9 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya 9
Da samũdãwa waɗanda suka fasa duwãtsu a cikin Wadi suka yi gidãje)?
وَفِرْعَوْنَ ذِي الْأَوْتَادِ ( 10 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya 10
Da Fir'auna mai turãku.
الَّذِينَ طَغَوْا فِي الْبِلَادِ ( 11 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya 11
Waɗanda suka ƙẽtare iyãkarsu, a cikin garũruwa?
فَأَكْثَرُوا فِيهَا الْفَسَادَ ( 12 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya 12
Sabõda haka, suka yawaita yin ɓarna a cikinsu.
فَصَبَّ عَلَيْهِمْ رَبُّكَ سَوْطَ عَذَابٍ ( 13 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya 13
Sabõda haka Ubangijinka Ya zuba musu bũlãlar azãba.
إِنَّ رَبَّكَ لَبِالْمِرْصَادِ ( 14 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya 14
Lalle ne, Ubangijinka Yana nan a mafaka.
فَأَمَّا الْإِنسَانُ إِذَا مَا ابْتَلَاهُ رَبُّهُ فَأَكْرَمَهُ وَنَعَّمَهُ فَيَقُولُ رَبِّي أَكْرَمَنِ ( 15 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya 15
To, amma fa mutum idan Ubangijibsa Ya jarraba shi, wãto Yã girmama shi kuma Ya yi masa ni'ima, sai ya ce: "Ubangijina Ya girmama ni."
وَأَمَّا إِذَا مَا ابْتَلَاهُ فَقَدَرَ عَلَيْهِ رِزْقَهُ فَيَقُولُ رَبِّي أَهَانَنِ ( 16 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya 16
Kuma idan Ya jarraba shi, wãto Ya ƙuntata masa abincinsa, sai ya ce: "Ubangijina Ya walãkanta ni."
كَلَّا ۖ بَل لَّا تُكْرِمُونَ الْيَتِيمَ ( 17 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya 17
A'aha! Bari wannan, ai bã ku girmama marãya!
وَلَا تَحَاضُّونَ عَلَىٰ طَعَامِ الْمِسْكِينِ ( 18 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya 18
Bã ku kwaɗaitã wa jũnanku ga (tattalin) abincin matalauci!
وَتَأْكُلُونَ التُّرَاثَ أَكْلًا لَّمًّا ( 19 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya 19
Kuma kuna cin dũkiyar gãdo, ci na tãrãwa.
وَتُحِبُّونَ الْمَالَ حُبًّا جَمًّا ( 20 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya 20
Kuma kuna son dũkiya, so mai yawa.
كَلَّا إِذَا دُكَّتِ الْأَرْضُ دَكًّا دَكًّا ( 21 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya 21
A'aha! Idan aka niƙa ƙasa niƙewa sosai.
وَجَاءَ رَبُّكَ وَالْمَلَكُ صَفًّا صَفًّا ( 22 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya 22
Kuma Ubangijinka Ya zo, alhãli malã'iku na jẽre, safũ- safu.
وَجِيءَ يَوْمَئِذٍ بِجَهَنَّمَ ۚ يَوْمَئِذٍ يَتَذَكَّرُ الْإِنسَانُ وَأَنَّىٰ لَهُ الذِّكْرَىٰ ( 23 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya 23
Kuma a ranar nan aka zo da Jahannama. A ranar nan mutum zai yi tunãni. To, inã fa tunãni yake a gare shi!
يَقُولُ يَا لَيْتَنِي قَدَّمْتُ لِحَيَاتِي ( 24 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya 24
Yana dinga cẽwa, "Kaitona, dã na gabatar (da aikin ƙwarai) domin rãyuwata!"
فَيَوْمَئِذٍ لَّا يُعَذِّبُ عَذَابَهُ أَحَدٌ ( 25 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya 25
To, a rãnar nan bãbu wani mai yin azãba irin azãbar Allah.
وَلَا يُوثِقُ وَثَاقَهُ أَحَدٌ ( 26 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya 26
Kuma bãbu wani mai ɗauri irin ɗaurinSa.
يَا أَيَّتُهَا النَّفْسُ الْمُطْمَئِنَّةُ ( 27 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya 27
Yã kai rai mai natsuwa!
ارْجِعِي إِلَىٰ رَبِّكِ رَاضِيَةً مَّرْضِيَّةً ( 28 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya 28
Ka koma zuwa ga Ubangijinka, alhãli kana mai yarda (da abin da Ya ƙaddara maka a dũniya) abar yardarwa (da sakamakon da zã a ba ka a Lãhira).
فَادْخُلِي فِي عِبَادِي ( 29 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya 29
Sabõbda haka, ka shiga cikin bãyiNa (mãsu bin umurui a dũniya).
وَادْخُلِي جَنَّتِي ( 30 ) Al-Fajr ( The Dawn ) - Aya 30
Kuma ka shiga AljannaTa (a Lãhira).
Facebook Twitter Google+ Pinterest Reddit StumbleUpon Linkedin Tumblr Google Bookmarks Email

Select language

Select surah